Hadisan Ma’aiki (SAW) waDanda suka tabbatar da mustahabbancin
yin tawassali da neman albarkan magabata.
Musulmi
ba shi da madogarar da ya fi Alqur’ani mai
girma, da Hadisin Manzon Allah (SAW)
a kan ko wace irin mas’ala ta shari’a, bayansu sai Ijma’i da qiyasi da shauran
masadir wadanda aka yi sa6ani a kai.
A
jawabinmu da ya gabata mun ga inda Allah Madaukakin sarki ya yi umurni da a yi
tawassuli zuwa ga reshi, a suratul Ma’idah aya ta (35) kuma mun ga wadanda ya
nuna tawassulinsu ba zai amfane masu yi ba zuwa ga Allah a Suratul Isra’i aya
ta (57) a duka ayoyin biyu mun kawo tafsirin wasu malamai a game da su.
A
game da Hadisai wadanda suke yin Magana a game da tawassuli da Ma’aiki (SAW)
a halin yana raye da bayan ya yi wafati, da yin tawassali da salihan bayin Allah,
suma a halin suna raye da bayan sun yi wafati, da neman albarkacinsu, da nau’o’in
su, duka wani lamari ne da za mu iya tabbatar da su da Hadisai ingattatu
mutawatirai, kamar yadda muka sha fadi cewa wadannan littafai na Tushen
Wahabiyanci a Nigeriya, ba mu buqatar su yi girma yadda mai karatu zai qosa,
don haka Hadisai kadan zamu kawo, wadanda malaman Hadisi suka tabbatar da
ingancinsu in Allah ya yarda.
A.
Tawassuli da Annabi Muhammadu (SAW).
Hadisai
ingantattu sun tabbatar da halascin yin tawassali da Ma’aiki (SAW)
ba tare da yin la’akari da cewa yana raye ne ko bayan ya yi wafati ne, hasali
ma Annabawa da yawa (A.S.) sun yi tawassali da shi kafin bayyanarsa.
1.
Hadisin Tawassalin Annabi Adam (A.S.)
da shi.
Shekh
Sayyid Muhammadu Al’alawiy, Almalikiy Alhusainy, daya daga cikin manyan Malaman
da suke karantarwa a masallacin Harami na garin Makka ya fada a cikin
littafinsa mai suna (مفاهيم يجب أن تصحح)
ma’anar sunan wannan littafi shine: “Nau’o’in fahimtar da suka zama wajibi a
kawo gyara a kansu”.
Daga
cikin fahimtar da akwai na inkarin yin tawassuli da Ma’aiki (SAW)
daga cikin Hadisan da wannan shaihun malami ya kafa hujja da shi na halascin
yin tawassuli da akwai Hadisin da Imamu Hakim (R.A.) ya ruwaito a cikin
littafinsa: (Al-Mustadarak) ga hadisin:
قال رسول الله صلى الله عليه وسلم:
لما اقترب آدم الخطيئة قال: يا رب أسألك بحق محمد لما غفرت لي، فقال الله: يا آدم
وكيف عرفت محمداً ولم أخلقه؟ قال: يا رب لأنك لما خلقتني بيدك ونفخت فيّ من روحك
رفعت رأسي فرأيت على قوائم العرش مكتوباً لا إله إلا الله محمد رسول الله، فعلمت أنك لم تضف إلى
اسمك إلا أحبّ الخلق إليك، فقال الله: صدقت يا آدم إنه لأحب الخلق إلي، ادعني بحقه
فقد غفرت لك ولولا محمد ما خلقتك".
أخرجه الحاكم في المستدرك وصححه،
ورواه الحافظ السيوطي في خصائص النبوة وصححه، ورواه البيهقي في دلائل النبوة وهو
لا يروي الموضوعات، وصححه أيضاً القسطلاني، والزرقاني في المواهب الدنية، والسبكي
في شفاء السقام.
Ma’ana:
“Manzon
Allah (SAW)ya ce: ya yin da
Adamu (A.S.) ya yi kuskuren – cin itaciya – ya ce: ya Ubangiji ina roqonka da
haqqin Muhammadu (SAW)da
ka gafarta mani? Sai Allah ya ce: ya kai Adam ya ya a ka yi ka san Muhammadu (SAW)
alhali ban riga na halicce shi ba? Sai – Adam (S.A.) ya ce: ya Ubangiji a
lokacin da ka halicce ni da hannunka ka hura mani rai daga ranka, sai na daga
kai na sama sai na ga ni a rubuce a kan turakun al’arshi “Lailaha illallahu
Muhammadur Rasulullah” sai na san lallai baka hada sunanka da wani sai na mafi
soyuwar halitta a wajenka, sai Allah ya ce: ka yi gaskiya ya Adam (A.S.) haqiqa
shi ne mafi soyuwar halitta a guna, tunda ka kirani da haqqinsa, don haka na
gafarta maka, saboda ba domin Muhammadu ba (SAW)
da ban halicce ka ba”.
Al-Hakim
ya fitar da wannan hadisi a cikin “Al-Mustadarak”, ya kuma tabbatar da
ingancinsa, Al-Hafiz Assuyudiy ya ruwaito shi a cikin “Khasa’isun Nubuwwa” ya
inganta shi, Al-Baihaqi ya ruwaito shi a cikin “Dala’ilun Nubuwwah” kuma an san
bai ruwaito – hadisai – mauduai, hakannan Al-Asqalani ya inganta shi , da
Az-Zarqani, a cikin “Al-Mawahibul Ladunniya” da As-Sabqi a cikin “Shifaus Siqam”.
Wannan
hadisi ingantacce ko da shi kadai muka samu ya isa a kafa hujja ga maqiya yin
tawassuli da Ma’aiki (SAW) wadanda
suka ce ba ayi sai da wanda yake raye, to sai gashi Annabi Adam (A.S.) ya yi
kamun qafa da shi kafin ma a halicce shi, balle kuma a ce yana raye, ko bayan
wafatinsa.
2.
Hadisin da Ma’aiki (SAW)
ya koyar da yadda za a yi tawassuli da shi:
Furofesa
Shekh Aliyu Jumah Mufti na qasar Masar ya amsa wata fatawa a game da yin
tawassuli da Annabi (SAW) a cikin littafinsa mai suna: (البيان لما يشغل الأذهان) Ma’ana: “Bayani a game da abubuwan da yake
Dau kan hankali” a wajen amsa fatawarsa a game da tawassuli ya kawo Hadisin da
aka kar6o daga Usman bin Hanifi cewa:
"أن
رجلاً ضرير
البصر
أتى النبي صلى الله عليه وسلم فقال: ادع الله لي أن يعافيني؟ قال: إن شئت دعوت وإن
شئت صبرت فهو خير لك، قال: فادعه. قال" فأمره أن يتوضأ فيحسن وضوءه ويدعو
بهذا الدعاء: "اللهم إني أسألك وأتوجه إليك بنبيك محمد نبي الرحمة، يا محمد
إني توجهت بك إلى ربي في حاجتي هذه لتقضي لي، اللهم فشفعه فيّ".
أخرجه
أحمد في مسنده، والترمذي في سننه، وقال هذا حديث حسن صحيح، والنسائي في الكبرى،
وفي عمل اليوم والليلة، وابن ماجه في سننه، والحاكم في المستدرك.
(قال الدكتور) ولا نعلم أحداً ضعفه
حتى في ذلك العصر الحديث ممن اشتهر بالمنهج التشديدي، فقد صححه الشيخ الألباني،
فليس هناك من يعترض على سند الحديث ولا متنه.
Ma’ana:
“Wani
mutum da ba ya gani sosai ya tafi wajen Annabi (SAW)
sai ya ce masa: ka roqan mani Allah ya bani lafiya, sai yace: in ka so zan roqan
maka Allah, in ka so kuma ka yi haquri ya fi maka alhairi, sai ya ce: ka roqe
shi, sai Manzon Allah (SAW)
ya ummurce shi da ya yi Al-walla, ya kuma kyautata alwallar, ya yi du’ai da
wannan addu’ar: ya Allah ina roqonka ina kuma fuskantarka da alfarmar Manzaon ka
Muhammadu Annabin rahma, ya Muhammadu ina fuskantarka da alfarmarka zuwa waje
Ubangijina a game da buqata ta wannan, ya Allah ka sanya cetonsa a gareni”.
Imamu
Ahmad ya fitar da wannan hadisin a Musnad Dinsa, da Tirmizi a sunan Dinsa ya kuma ce hadisi ne mai kyau, kuma
ingantacce ne, da An-nasa’i a cikin Al-Kubra, da kuma Amalil – yam-Wallailih,
da Ibin Majah a cikin sunan Dinsa da Hakim a cikin Al-Mustadrak.
(Babban
Malami Dr. Aliyu Juma) ya ce: ba mu san wani wanda ya raunana wannan hadisin
ba, har a wannan zamanin daga cikin waDanda suka yi fice wajen yin tsanani a
manhajarsu, har da Shaihu Al-Albaniy ya inganta wannan hadisi, hasali babu wani
da aka samu ya soki masu ruwaito shi, ko ya soki mataninsa.
Idan
muka lura da wannan hadisi ingantacce, za mu ga Ma’aiki (SAW)
ne da kanshi yake karantar da yadda za a yi kamun qafa da shi a wurin Allah,
domin kai wa ga biyan buqata, don haka wani Dan Bidi’an zai zo bayansa da
shaikaru Dari bakwai, ya ce mana ba a yin kamun qafa da shi mu saurare shi?
3.
Hadisin yin Tawassuli da Ma’aiki (SAW)
bayan wafatinsa:
Shaihul
Azhar (Rahimahul lahu) Jadul-Haq Aliyu Jadul-Haq ya tabbatar da mustahabbancin
yin tawassuli da Annabi (SAW) bayan wafatinsa, a
cikin littafinsa mai suna(بيان
للناس) da Hadisin da Imamu Al-Baihaqi ya ruwaito mai cewa:
" روي البيهقي في " دلائل
النبوة" أن قحطاً أصاب الناس في زمن عمر، فجاء رجل قبر النبي صلى الله عليه
وسلم فقال: يا رسول الله، استسق الله لأمتك فإنهم قد هلكوا، فأتاه الرسول في
المنام، فقال: ائت عمر فاقرئه السلام واخبره أنهم مسقون، وقل له: "عليك الكيس
الكيس" فأتى الرجل عمر فأخبره فبكى، وقال: يا رب ما آلو إلا ما عجزت عنه،
يعني لا أقصر إلا فيما عجزت عنه".
قال شيخ
الأزهر: (في الحاشية) اسناده صحيح كما قال ابن كثير في البداية، وروي مثله ابن أبي
شيبة، وقال ابن حجر في فتح الباري: "اسناده صحيح".
Ma’ana:
Al-Baihaqi ya ruwaito
a (Dala’ilun -Nubuwa) cewa: Fari ya aukawa mutane a zamanin sayyadina Umar
(R.A.) sai wani mutum ya zo qabarin Annabi (S.A.W) ya ce: ya Manzon Allah ka roqi
Allah ya shayar da al-ummarka, saboda sun hallaka, sai Manzon Allah (SAW) ya zo ma-wannan
mutumin-a mafarki ya ce ma shi je ka wajen Umar ka yi masa sallama sannan kuma
ka ba shi labari cewa za a shayar da su ruwan sama, kuma ka faDa ma shi cewa:
“Ina horonka da matuqar hankalta” sai mutumin –da ya farka- ya je wajen Umar
(R.A.) ya ba shi labarin, sai Umar ya fashe da kuka, ya ce: ya Ubangiji ba zan taqaitaba sai inda qarfina
ya qare, Ma’ana ban taqaituba, sai a cikin abin da na gajiya ga yinsa”.
Shaihul
Azhar (R.A.) ya faDi a Hashiya cewa Isnadin – wannan Hadisi – ingantacce ne
kamar yadda Ibun Kasir ya faDa a cikin Al-Bidaya, kamar yadda Ibni Abi Shaibata
ya ruwaito kwatankwacinsa, Ibnu Hajar ya faDa a cikin Fatahul- Bari cewa:
Isnadinsa ingantacce ne.
Hadisai
ingantattu a littatafan Hadisai masu yawa, sun ba mu labarin cewa a lokacin da
Ma’aiki (SAW) yake raye idan an sami fari an sha
zuwa ana kama qafa da shi ya roqi Allah a sami ruwa, don saboda kar a zaci cewa
bayan wafatinsa ba shi da wani tasiri, saboda haka wannan bawan Allah wanda ya
yi imani da cewa Ma’aiki (S.A.W) a cikin qabari yana roqan Allah ya amsa kamar
yadda yake mayar da sallama ga duk wanda ya yi masa, sai ya tafi ya yi kamun qafa
da shi, Khalifansa na biyu sayyadina Umar (R.A.) wanda abin ya faru a
zamaninsa, bai qaryata ba sabo da sanin matsayin Ma’aiki (SAW) hasali
na dama ma ya yi da cewa shi ya kamata a ce ya yi haka.
Wannan
hujja ne mai gamsarwa da take tabbatar da neman du’ain Ma’aiki (SAW)
don yayewar wani bala’i a tsakanin al’ummarsa, ‘ya Rasulullahi, muna kamun qafa
da kai zuwa ga Allah ya shiriyi musulmi masu tauye maka haqqi’, ako ina suke.
4.
Hadisin yin Tawassuli da Ma’aiki (SAW)
a ranar gobe {iyama:
Imamu
Buhari da Imamu Muslim da Imamu Trimizi da Imamu Ibin Majah da Imamu Darami
Allah ya yarda da su duk cikansu sun ruwaito wannan hadisi mai tsawo na yin
tawassuli da Ma’aiki (SAW) a ranar tashin qiyama.
Ga
abin da Imamu Buhari ya ruwaito a
Kitabul Fathul Bari sharhin Sahihul Buhari Mujalladi na (13) shafi na (573)
bugun: “Darul Manar”
عن
أنس أن النبي صلى الله عليه وسلم قال: يجمع الله المؤمنين يوم القيامة فيقولون: لو
استشفعنا إلى ربنا حتى يريحنا من مكاننا هذا، فيأتون آدم فيقولون: يا آدم أما ترى
الناس؟ خلقك الله بيده، واسجد لك ملائكته، وعلمك أسماء كل شيء، اشفع لنا إلى ربك
حتى يريحنا من مكاننا هذا فيقول: لست هناك – ويذكر لهم الخطيئة التي أصاب – ولكن
ائتوا نوحاً فإنه أول رسول بعثه الله إلى أهل الأرض، فيأتون نوحاً فيقول: لست هناك
– ويذكر خطيئة التى أصاب، ولكن ائتوا إبراهيم خليل الرحمن، فيأتون إبراهيم فيقول:
لست هناكم – ويذكر لهم خطايه التي أصابها – ولكن ائتوا موسى عبداً أتاه الله
التوراة وكلّمه تكليماً، فيأتون موسى موسى فيقول: لست هناكم – ويذكر لهم الخطيئة
التي أصابها – ولكن ائتوا عيسى عبد الله ورسوله وكلمته وروحه، فيأتون عيسى فيقول:
لست هناكم، ولكن ائتوا محمد صلى الله عليه وسلم عبداً غفر له ما تقدم من ذنبه وما
تأخر، فيأتونني، فأنطلق، فاستأذن على ربي فيؤذن لي عليه، فإذا رأيت ربي وقعت له
ساجداً، فيدعني ما شاء الله أن يدعني، ثم يقال لي: ارفع محمد قل يسمع، وسل تعطه،
واشفع تشفع، فأحمد ربي بمحامد علمنيها، ثم أشفع.........
Ma’ana:
An karbo daga Anas (R.A.)
cewa Ma’aiki (SAW)ya ce:A ranar Al-qiyama, Allah yakan tara-hankalin – muminai sai su
ce: me zai san ya ba za mu yi kamun qafa ba zuwa ga Ubangijin mu, don ya hutar
damu daga wannan hali da muke ciki, sai su tafi wurin Adam (A.S.) su ce masa:
ya Adamu baka ganin halin da mutane suke ciki? Kai ne fa Allah ya halicceka da hannunsa
- ba Uwa ba Uba mala’iku suka yi
ma sujjada, - Allah – ya sanar da kai sunan komi da komi, kayi mana ceto mana a
wurin Ubangijinka domin ya hutar damu daga wannan hali da muke ciki – na dogon
tsayuwa da a zaba- sai – Adam (A.S) – ya ce: ai bani da ikon yin haka – ya faDa
masu kuskuren day a yi (na cin itaciya) – sai dai ku tafi wurin Nuhu (A.S.)
wanda shine farkon Manzo da Allah ya aiko a bayan qasa, sai – Jamaa – su tafi
wurin Nuhu (A.S.) – su faDa masa abin da
yake tafe da su – sai ya ce: bani da iko – ya gaya ma su kuskuren da ya aikata
(na roqon Allah ya hallaka al’ummarsa waDanda suka qi binsa) amma ku tafi wurin
Ibrahim maji daDin Ubangiji, sai su tafi wurin Ibrahim (A.S.) – su gaya masa buqa
tarsu – sai ya ce: bani da iko – ya gaya masu wasu kurakurai da ya aikata (na
yin qarya don karantarwa) sai dai ku tafi wurin Musa (A.S.) wanda bawane wanda
Allah ya ba shi littafin attaura, ya kuma yi zance da shi, sai su tafi wurin Musa
(A.S.) – su faDa masa
abin da yake tafe dasu – sai ya ce: bani da iko- ya faDa masu kura kuren da ya
aikata (a wurin ceto da yin gwaninta) sai ya ce: masu amma ku tafi wurin Isah
bawan Allah Manzonsa, Kalmarsa, Ruhinsa, sai su taho wurin Isah (A.S.) sai ya
ce: masu bani da iko, sai dai ku tafi wurin Muhammadu (SAW)wanda shi bawane da
Allah ya gafarta masa zunubansa gabaki Daya, sai su taho wuri na- su faDa mani
buqatun su – sai na tafi na nemi izinin saduwa da Ubangijina, sai ya bani
izini, sai na ga Ubangijina, sai na faDi na yi masa sujjada, sai ya ajiyeni a
inda ya so ajiyeni, saannan ya ce mani Daga kai Muhammadu, ka faDi a saurareka,
ka tambayi – abin da ka keso- a ba ka, ka nemi ceto a baka ceto, sai na yabi
Ubangijina da duk wani yabo da ya sanar dani, saannan sai na yi ceto…………
Wannan
hadisi mai tsawo, wanda duk malaman hadisi sun inganta shi, dukanin alummar
musulmi a duk inda suke a doniya, sun yarda da cewa Annabi Muhammadu (SAW)
zai nemi a bashi ceto a ranar tashin al-qiyama wanda ake kira (الشفاعة العظمى) kuma Allah MaDaukakin Sarki zai bashi,
wannan ceto har Wahabiyawa na Saudiya sun yarda da a kwaita, amma abin mamaki a
nan qasar tamu ta Najeriya sai da aka sami wasu 6angare na ‘yan Izala almajiran
malam Abubakar Gumi, waDan da suka fito suka qaryata batun yin kowane irin ceto
a ranar qiyama, a yayin da aka sami wasu kuma suna tabbatar da cewa da akwai
ceto a Lahira suka dosa kiran taro ya su - ya su kan wannan mas’ala suna
kafirta juna, har sai da magana ta kai gaban Malam.
A
jaridar Gaskiya tafi kwabo ta ranar Asabar (24) ga watan Nuwanba, 1991 bugu ta
(5,125) a shafi na farko- mai Dauke da hoton Malam Abubakar Gumi – ga abin da
aka rubuta: “DUK WANDA YA CE BA CETO KO AZABAR
{ABARI YA YI RIDDA in ji Gumi”.
Idan
ana neman qarin bayani sai a nemi wannan jarida a karanta, zaa ga inda malamin
ya tabbatar da cewa za a yi Tawassuli da Ma’aiki (SAW)
a ranar qiyama, kuma a bashi, haka nan yace ana baiwa Annabawa da Mala’iku, da Waliyyai
ceto a wannan ranar, idan Allah ya yi masu izini.
Amma
bari kuji irin martanin da wani babban almajirinsa na biyu a majalisar tasa,
irin amsar da ya bayar da aka tambayeshi a game da wannan jawabi na malamin
nasa:
Tambaya: Maganar
ceto shin me ya sa mutane su ke damuwa a kanta?
Amsa: “Masu neman ceton nan su aka aiko ma
Annabawa don su faDa masu, maganar ceton nan, mu mun yi imani Allah kaDaine me
ceto kuma ceton nan ga hannun Allah yake, kuma Allah yana ceton wanda ya so,
daga cikin rahamanshi, amma cewa wasu mutane za su yi ceto, ko Annabawa za su
yi ceto da sauransu dai to waDan nan maganganune wanda mushurikai sun ka faDi
tun da daDewa, maganganune na mushurikai suke biyan wasu masu cewa, don haka
cewa akwai wasu masu ceto, to ga addinin musulunci ya nuna mana babu wani mai
ceto sai Allah, maganan ceto Dinnan dama can mushurikai ana faDa dasu akan
ceto, don haka duk wanda kaji ya shake fuska ya shake murya yana cewa a kwai
ceto, zaa yi ceto, to jinin mushurikai yake yawo cikin jikin shi, ceton nan
babu wanda kayi nai sai Allah….)
muna da cikakken wannan bayani a kaset
na firarrakin da aka yi da wannan malami almajirin Abubakar Gumi, koda shike
daga baya ya ce shi ba almajinrinsa bane da karatunsa Gumi ya ganshi.
Daga
wannan jawabi nasa zamu fahimci shima Abubakar Gumin ya zama mushuriki don haka
shi ma gara Kirista da shi, kamar yadda ya ce: “Gara Kirista da dan dariqa” don
ya yarda da ceto a lahira, inji
almajirinshi.
B.
Tawassuli da Bayin Allah nagari:
Kamar
yadda mu ka kawo hadisai ingantattu masu yawa waDanda suka tabbatar da yin
tawassuli da Ma’aiki (SAW) tun kafin ya fito duniya, ta yadda
Annabawa da ban- da ban suka rinqa yin kamun qafa da shi a wurin Allah, kuma
Allah ya sauraresu ya biya masu buqata, haka nan za muga hadisai ingantattu da
suka tabbatar da yin tawassuli da shi yana raye da tun kafin ya zama Manzo, da
bayan ya zama Manzon Allah (SAW) hadisan da har dan Taimiyya
ya yarda dasu, inda aka sami sa6ani a hadisan yin tawassuli da shi bayan ya yi
wafati waDanda malamai masu yawa sun tabbatar da ingancin su fanDarewar sa da
na mabiyan sa, ba zai dame mu ba.
A
wannan babi zamu dubane, ko suma Salihan Bayi zaa iya yin tawassuli dasu kamar
yadda aka yi da Ma’aiki (SAW) a halin suna raye da
bayan sun yi wafati, sabo da kasancewarsu khalifofinsa ko magadansa, zai yiwu a
yi kamun qafa dasu, a halin suna raye da bayan sun yi wafati?
1.
Hadisin da ya yi umurni da ayi
tawassuli da wani bawan Allah idan ya bayyana:
Uwaisul
qarni wanda shi ba Sahabibane Tabi’ine, amma
sai ga shi Ma’aiki (SAW) ya na ummurtan Sahabai harma da waDanda
aka yi masu bishara da shiga Aljanna, da cewa idan sun sadu da shi su yi
tawassuli da shi ta neman ya yi masu du’ai, ga dai abin da hadisin yake cewa:
عن
أُسير بن جابر قال كان عمر بن الخطاب إذا أتى عليه أمداد أهل اليمن سألهم أفيكم
أويس بن عامر؟ حتى أتى على أويس، فقال: أنت أويس بن عامر؟ قال: نعم، قال: من مراد
ثم من قرن؟ قال: نعم، قال: فكان بك برص فبرأت منه إلا موضع درهم؟ قال: نعم، قال:
لك والدة؟ قال: نعم، قال: سمعت رسول الله صلى الله عليه وسلم يقول: يأتي عليكم
أويس بن عامر مع امداد أهل اليمن من مراد ثم من قرن كان به برص فبرأ منه إلا موضع
درهم له والدة بها بر لو أقسم على الله لأبرّه فإن استطعت أن يستغفر لك فافعل
فاستغفر لي فاستغفر له".
رواه مسلم في كتاب فضائل الصحابة، باب من فضائل أويس القرني
رضي الله عنه.
Ma’ana:
“An
kar6o daga Usairu Dan Jabir ya ce: Umar Dan KhaDDabi (R.A.) ya kasance ya na
tambayar gungun mutane Yaman- in sun zo – a cikinku da a kwai Uwaisu Dan amir?
Har zuwa lokacin daya haDu da Uwaisu, sai ya tambaye shi ya ce: kaine Uwaisu Dan
Amir? Ya ce: na’am, ya ce: daga murad? Sannan kuma daga qarnu? Ya ce: na’am,
sai ya ce: da ka zama kana da kuturta, sai ka warke, sai Dan wurin da bai wuce
faDin dirhamiba, ya ce: na’am, sai ya ce: kana da mahaifiya? Ya ce: na’am, sai
– sayadina Umar – ya ce: naji Ma’aiki (SAW)yana
cewa: Uwaisu Dan Amiru zai zo maku tare da wata tawagar mutanen Yamen daga
murad, sannan daga qarnu, ya kasance yana da cutar kuturta sai ya warke sai Dan
wani wuri mai faDin dirhami, ya na da mahaifiya wanda yake mata biyayya, da zai
rantse akan Allah – zai yi wani abu – ba zai bashi kunyaba, idan – mutun- ya
sami ikon neman ya roqa maka gafara ka nema, - don haka – ka roqamani gafara,
sai ya roqa masa”.
Imamu
Muslim ya ruwaito wannan hadisi a littafin falalar Sahabai, a cikin Babin
falalar Uwaisul-qarni (R.A.)
Wannan
hadisi idan muka koma ka’ida ta Usulul-Fiqh, bayan ya tabbatar mana da halascin
yin tawassuli da bawan Allah na gari don samun albarka du’ainsa, a wajen
isharar nassin zaa fahimci a bubuwa da yawa:
·
Tabbatar da cewa Ma’aiki (SAW)
ya san gaibi don gashi ya bayar da labarin zuwan mutumin da ba su yi zamani
tare da shi ba, babu shakka mai Ishiriniya ya faDi gaskiya a inda yake cewa:
بصير بسر
الغيب قبــــل كيانه * له يقرب المرمى وترتفع الحجب
Ma’ana:
Ma’aiki
(SAW)masanine na asirin da
yake 6oye kafin ya bayyana.
Da
shi ne ake kusantan abin guri, sa’annan akawar da ko wane irin shamakai.
·
Hakanan mun fahimci cewa zaa iya samun
bayin da Allah ya yarda dasu a ko wace
irin jinsi na mutane, kuma a ko wani zamani kamar yadda Ma’aiki (SAW)
ya ke cewa:
"مثل أمتي مثل
المطر لا يدري أوله خير أم آخره"
Ma’ana:
“Kwatankwacin
Alummata kamar ruwan samane, baa saniba na farkone yake Dauke da alhairi, ko na
qarshensa”, Imamu Tirmizi ya ruwaito wannan hadisi.
·
Hakanan zamu fahimci cewa daga cikin
abin da ya kai shi ga samun wannan matsayi shine biyayya ga mahaifiya “bai kasance a cikin irin mutanen da
sukan sayi qwaryar Nono su kai mataba, don su biya ta nonon da ta shayar
dasu domin kada tayi masu gori”.
·
Har ila yau muna iya fahimtar cewa
wannan hadisi maida martanine ga masu cewa sun fi qarfin su sanya wani malami
ya roqa masu Allah, don ba a fisu kusa das hi ba, kamar yadda muka ji ana fira
da wani Tsohon mai sarauta Dan Izala a kafan watsa labarai yana yin al-fahari
da cewa shi bai sanya wani malami ya roqa masa Allah – Allah ya shiryeshi – shi
bai san har Ma’aiki (SAW) ya gayama Sayyadina Umar (R.A) lokacin
da zai je umra cewa:"لا
تنسانا يا أخي من دعائك" Ma’ana: “Kar ka manta damu cikin du’ainka
ya Dan Uwa”.
2.
Hadisin da akai kamun qafa da Abbas
(R.A.):
An
sami hadisai ingantattu masu yawa waDanda suka tabbatar da cewa sau da yawa
idan an sami fari (rashin ruwa) a kan zo a yi kamun qafa da Ma’aiki (SAW)
zuwa ga Allah domin samun ruwa, sabo da kar a zaci yin haka ya ke6anta ne kawai
da shi Ma’aiki (SAW) sai Sayyadina Umar (R.A) a lokacin
Khalifancinsa da aka sami fari, Sabo da kar a zaci cewa sabo da Manzon Allah (SAW)
ya yi wafati babu shauran yin kamun qafa da wani, sai ya yi tawassuli da
sayyadina Abbas (R.A) qanin mahafin Ma’aiki (SAW)
don a sami ruwa.
Ga
hadisin da Imamu Buhari (R.A) ya ruwaito a sahihinsa a kitabul Istiqa’i:
"عن
عمر بن الخطاب رضي الله عنه أنه إذا اقحطوا استسقى بالعباس بن عبد المطلب رضي الله
عنه فقال: اللهم إنا كنا نتوسل عليك بنبينا فتسقينا وإنا نتوسل إليك بعمّ نبينا
فاسقنا، قال: فيسقون".
Ma’ana:
“An kar6o daga Umar Dan
Khaddab (R.A) ya na cewa: Idan an yi mana fari mukan nemi-Allah ya shayar damu-
da Abbas Dan Abdul Muddalib (R.A) sai yace: Ya Allah mun zama muna masu yin
tawassuli zuwa gareka da Annabinmu kana shayar damu, ayau muna masu yin
tawassuli zuwa ga reka da qanin Mahaifin Annabi (SAW)ka shayar damu, sai
yace: sai a ka shayar da su”.
Wannan
hadisi ingantacce wanda Imamu Buhari ya ruwaito a sahihin littafinsa ko shi kadai
ya isa ya tabbatar mana da cewa ana yin tawassuli da wani bawa na Allah, ya na
rayene ko bayan ya yi wafati, wasu su kance ai dama sun yarda idan mutum ya na
raye za a iya yin kamun qafa dashi zuwa ga Allah amma idan ya rasu ne ba’a yi
sabo da wannan hadisi.
Malamai
da yawa sun yi raddi a game da wannan mummunar fahimtar domin ai Allah a ke roqo
ya yi abin sabo da matsayin wani bawa nasa, a wurin shi, tawassuli da du’ain
wani bawan Allah ne sai idan yana raye ne za ka nema ya yi maka.
Sabo
da wadannan dalilia da muka samu daga dan Khaddabi (R.A) da tawassulinsa da
Uwaisul qarni, da tawassulinsa da Abbas (R.A) bai kamata mu barsu don maganar dan
Taimiyya ko dan Abdul-Wahab ba, ko dan Mahmud Gumi ba.
3.
Hadisin yin Tawassuli da duk wani mai
roqon Allah:
Saboda
Ma’aiki (SAW) ya nuna mana cewa babin wadan da ake
yin tawassuli dasu abune mai fadi, sai shi da kansa ya koyar da yin tawassuli
da wasu bayin Allah.
Imamu
Ibin Majah ya ruwaito wani hadisi a cikin sunnarsa a babin (المشي إلى الصلاة) Tafiya zuwa Masallaci, wanda yake cewa:
"عن
أبي سعيد الخدري قال: قال رسول الله صلى الله عنه وسلم: من خرج من بيته إلى الصلاة
فقال: اللهم إني أسألك بحق السائلين عليك، وأسألك بحق ممشاي هذا فإني لم أخرج
أشراً ولا بطراً ولا رياءً ولا سمعة وخرجت اتقاء سخطك وابتغاء مرضاتك فأسألك أن
تعيذني من النار، وأن تغفر لي ذنوبي إنه لا يغفر الذنوب إلا أنت، أقبل الله عليه
بوجهه واستغفر له ألف ملك".
Ma’ana:
An
kar6o daga Abu Saidul- Khudri ya ce: Manzon Allah (SAW)ya
ce: wanda ya fita daga gidansa zuwa masallaci sai yace: Ya Allah ni ina mai roqonka
don alfarman masu roqonka da kuma alfarmar tako na wannan, domin banfito don
sharri ba, ko don girman kai ba, ko sabo da riya, ko don Jida kai, na fitone
don tsoron hushinka, da neman yardanka, ina mai roqonka ka tsamar dani daga
wuta, ka kuma gafarta mani zunubaina, domin babu wani mai gafartawan zunubi sai
kai, Allah zai fuskance shi da fuskarsa, kuma Mala’iku dubu za su neman masa
gafara”.
Wannan
hadisi yana tabbatar mana da cewa mustahabine ga musulmi ya yi tawassuli zuwa
ga Allah da duk wani bawan Allah mai roqon Allah a duk inda ya ke.
neman albarka da wasu ababe
na Ma’aiki (SAW)
Yana daga cikin sunna mai kyau a nemi albarkan Ma’aiki (SAW) da duk wani abu da ya ji6ince shi.
Sau da yawa mukan karanta a cikin littafai na Wahabiyawa,
kamar yadda mu kan ji ta bakin ‘yan qungiya suna cewa: neman albarka da wani
abu na Ma’aiki (S.A.W) ko na wani Salihin bawa Waliyyi, shirka ne domin kanuna
abin yana da tasiri kenan ba Allah ba a cewarsu.
Don mu nuna ma “‘yan Izala ‘yan bidi’a” cewa abin
ba haka bane, a wannan babi zamu kawo maku Hadisai, da bayanai waDan da suka
tabbatar da cewa sunnace a musulunci a nemi tubarraki da wani abu na Ma’aiki (SAW) da na wani Salihin bawa, kamar yadda ake yin tawassuli
da su don samun biyan buqata, Sahabbai (R.A) sune suka fara sai tabi’ai, sai tabiut
tabiina abin yacigaba harya kawo kanmu, ba mune ‘yan dariqa muka faraba,
sunnace wadda muka gada daga bayin Allah nagari, Salafus salih, ko da yake ku
salafus saleh a wajen ku shine Dan Taimiyya da almajiransa.
dan bid'a ga dogon rubu babu ma'ana sai kame kame
ReplyDelete