Thursday, August 2, 2012

Gabatarwa (4) Abubakar Gumi ya warware alkawari

    Abubakar Gumi ya warware alkawari
Daya daga cikin Malaman da aka yi wadannan zama dasu Shaykh Sharif Ibrahim Saleh Maiduwuri, Allah ya ja kwanana, ya rubuta a wani littafi nasa na Larabci mai suna"المغير" a mukaddima shafi na (29) ga fassarar a cikin Hausa: daga cikin sharuddan da a ka gindaya a karshen wannan taro a Sokoto sune: kada wani daga cikin malaman ya yi gaban kansa wajen buga ko yada abubuwan da a ka gabatar a wurin zaman  da a kayi. amma da Malam Abubakar Gumi ya dawo Kaduna sai ya warware alkawari ya tarjama nasa jawabin zuwa Hausa, ya yada ta ta Gidan Rediyon (B.B.C) London (Musulunci da abin da ya ke warware shi) daga cikin abin da ya ke warware musulunci akwai karanta (Salatul Fatihi) saboda – a cewar sa - Shaihu Ahmadu Tijjani yana fifitata akan karanta Alkur’ani”.
Wannan shine dalilin da ya sa shima  Shaykh Sharif Ibrahim Saleh ya buga nasa littafin da ya kaddamar a wurin taron mai suna:
"التكفير أخطر بدعة تهدد السلام والوحدة بين المسلمين في نيجيريا".
Wanda aka buga shi kamar yadda a ka kaddamar da shi a Larabcen shi, haka shi ma Shaykh Malam Nasiru Kabara ya yi, ganin Malam Abubakar Gumi - Almajirinsa- ya warware alkawari a kan abin da aka cimma, sai shima ya sa aka buga Littafin da ya kaddamar a wurin taron mai suna"حقيقة التصوف الإسلامي".
Haka Gwamnatin Soja ta Obasanjo da Shehu Musa ‘yar Aduwa ta shude ba ta iya magance sabanin da Malam Abubakar Gumi ya haifar ba a wannan kasar na sai an koma kan akidar dan Abdul Wahab a nan Najeriya sannan za a zauna lafiya.
Wannan ittifaki na malamai wanda aka yi a sokoto a shekara ta (1979) a gaban mai alfarma sakin Musulmi  Abubakar na Uku, an sake yi  bayan shekaru biyar a Yankari ta jihar Bauchi a shekarar (1983) a gaban Mai Martaba  shehun Borno Alhaji Mustapha  Umar El-Kanemi, inda aka sake cinma matsaya a tsakanin malamai, wanda har aka kai gaban shugaban kasa  Alhaji shehu shagari ya albarkaci lamarin.
Hakanan Malamai sun sake zama don jaddada wannan ittifaki, a shekarar (1988) a garin Kaduna a gaban Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Ado Bayero. Ga wani yanki na jawabin bayan taron:
za mu ci gaba.....

4 comments:

  1. ALLAH YA SHIRYE SHARIFF SALEH YA DAINA WANNAN MUMUNAR AQEEDAH TA SUFAYE

    ReplyDelete
  2. Enter your comment..allah yajaa zamaninka kuci gabada warware mana gaskiya.

    ReplyDelete