DUBA YANDA
ZA A SAMI MATSAYA A 1977/ 78:
Ganin yadda abubuwa su ke ci gaba da tabarbarewa, da rashin kwanciyar
hankali sai Gwamnan Jihar Kaduna na wannan lokacin Group Kaftin Usman
Jibirin ya yi kokarin shirya wani zama don yin nazarin abubuwan da suke kawo sabani
a tsakanin Malam Abubakar Gumi da malaman darika, a shekara ta (1977) amma
Malam Abubakar Gumi sai ya ki yarda, ya ce ya sami labarin a na barazanar
hallaka shi a wurin zaman.
Mai yiwuwa ganin wannan yunkuri da Gwamnar Jihar Kaduna ya yi ya ci
tura, shi ya sanya Gwamnatin Tarayya a karkashin jagorancin Janaral Obasanjo
ita ma ta yi kokarin kira taron malamai a shekara ta (1978) don duba matsalolin
da su ke kawo rigimar addini a tsakanin Musulmi da Musulmi masamman kungiyar
Malam Abubakar Gumi da mabiyansa.
A wata majiya mai tushe an ce dalilin kiran taron
shine bayan da a ka sauke Malam daga Alkalin Alkalai na Jahohin Arewa sai ya bukaci
a nada shi mufti na Tarayyar Najeriya, kamar yadda a ke yi akasashen Larabawa,
wanda duk wata matsala da ta shafi Musulmi sai abin da ya ce, sai Gwamnatin
Obasanjo ta amince da haka, sai kuma ga wata tawaga ta jagororin al’umar
musulmi daga jahohin Arewa bisa
jagorancin wani babban alkali a Kano suka tafi suka sami Shugaban kasa Obasanjo
suka nuna amincewar su na nada ma su mufti amma ba su yarda a baiwa Malam
Abubakar Gumi ba, an ce wannan shi ne dalilin da ya sanya Gwamnatin Tarayya ta
kafa kwamiti na Malamai don warware matsalar rashin jituwa da a ke samu, a karkashin
jagorancin Mataimakin Shugaban kasa Janar Shehu Musa ‘Yar Aduwa, Allah Ya ji kansa,
amin
Kwamitin Malaman ya zauna a Ikko da Sokoto kuma a
karshe ya fitar da sakamako wanda Malaman suka hadu a kai, wanda ya nuna alamar
samuwar zaman lafiya da hadin kai a tsakanin al'ummar Musulmi da fahimtar juna,
amma sai malam Abubakar Gumi ya
warware alkawari daga baya.
A wata takarda da aka fitar a karshen taro wanda
Mai alfarma Sarkin Musulmi Abubakar III – Allah ya gafarta masa- ya sa wa hannu
a ranar 5/3/1979 ga abin da ta kunsa:
Matsaya kan taron Mallamai Gaban Sarkin Musulmi
EMC/S/082/Vol.
III/285.
Sultan's Palace
Sokoto.
5th March, 1979
Assalamu
Alaikum.
Bayan haka ina sanarsheku wani
Kwamitin Malamai da aka kafa don su
binciki bam- bance-bambance da ke tsakanin Musulmi a kasarnan, sun yi taro biyu a Ikko: daya a cikin watan Oktoba,
1978, na biyu kuma daga 3-5 ga watan Fabrairu, 1979. Wannan Kwamitin ya kumshi
Alhaji Nasiru Kabara, Alhaji Abubakar Mahmud Gummi, Alhaji Isma'ila Ibrahim,
Alhaji Sharif Ibrahim Saleh da Alhaji Muntaka Coomassie.
Malaman sun hadu da niyya ta kwarai ta
neman abinda zai kawo jituwa da Maslaha tsakanin Musulmi gaba daya.
Malaman sun rubuta abinda fahimtarsu
ta nuna masu game da musulunci da darikokin Sufaye?An karanta bahasin
kowane malami an kuma yi Munakasha" tasa.
Malaman sun yarda cewa dukkan littafan
da aka rubuta a kowane fanni za'a sami sahihi a cikinsu, ta yiwu kuma a sami
kuskure a cikinsu. Saboda haka ya fi kyau
a bar binciken wadannan littatafai. Sai kowane malami kwararre a cikin
fanninsa ya tsaya akan wannan fanni. Malaman sun yarda cewa littafan sufaye an
rubuta su ne saboda sufaye; don haka bai kamata a bincike su ba muddin dai ba
a san fanninsu ba. Kuma bai halatta a gusar da barnar da za ta jawo wata barnar
da ta fita ba. Haka kuma duk wanda ya gayawa dan uwansa cewa shi kafiri ne, to,
dayansu ne kafiri. Saboda haka ya kamata duk wata hanya da za ta kawo haduwar kan musulmi a karfafa
ta.
Malaman
kuma sun yarda cewa darika ba wajiba bace amma-
neman mai shiryarwa ga addini wajibi ne, domin samun mai shiriya da kansa nadiri
ne. Haka kuma malaman sun yi ittifakia kan cewa Hadisin nan wanda a
cikinsa mala'ika Jibrilu ya zo ya tambayi Annabi ma'anar Musulunci da Imani da
Ihsani ya kumshi abubuwa uku: (i) Ma'anar Musulunci,(ii) Ma'anar Imani, (iii)
Ma'anar ihsani. Fannin ilmin da yake bayanin Islam shi ake kira fikhu.
Fannin da yake bayanin lmani shi
ake cewa Ilm-al-tawhid wa al-kalam. Fannin
da yake binciken Ihsani shi ake
cewa tasawwuf kuma abubuwan da suka rassanta daga gare shi na wuruddai
ko azkaru su ne darika. Haka kuma malamai sun yi ittifaki a kan zo
ga Annabawa ko ta wane hali ne, to duka hukumcinsa daya ne. Wahyi da a yi abu
ko a bari ga
shari'a ya kebanta ne ga Annabawa kurum. Amma ilhami na waliyyai fahimta ce
daga Allah wadda ba ta kunshi wani sabon hukumci na shari'a ba. ma'anar wahyi. A
cikin littafi "Fara'id al-jallah" ne Shehu Abdullahi Gwandu, an sami
bayanin cewa wahyi yana zama ta hanyar mala'ika ko ta ilhami ko cikin barci ko
cikin wata takarda. In wahyi ya
Haka kuma malamai sun yarda cewa da'awar annabci shine kafirci amma da'awar ilhami
ba kafirci ba ne. Sun yi ittifaki
a kan
cewa mafarki ya kasu gida uku: (i) Akwai mafarki daga Allah wanda kuma abinda
ya kunsa ya dace da abinda ya zo daidai da shari'a. (ii), Akwai mafarki wanda
yake labarin rai ne; (iii) akwai kuma mafarkin da abirida ya kunsa ya zo ne
daga Shaidan. Malamai sun yarda da cewa Annabi ya ce: “Annabci ya kare sai dai mubashsharat", watau mumini ya
ganarwa kansa wani alheri a mafarki ko kuma ganar masa.
Haka kuma malaman
sun ba da shawara ga musulmi cewa su koyi addininsu, su yi aiki da Kur'ani da Hadisi bisa ga
fassarar da malaman sunna suka yi. Kuma
su bar saurin kafirta juna ga mas'alolin
da aka yi sabanin fahimta a kansu. Su zama kamar yadda Allah ya
umurce su da cewa:
واعتصموا بحبل الله جميعا ولا تفرقوا
watau ku kankamewa igivar Allah gaba dayanku,
kada ku rarrabu.
Haka nan kuma malaman sun ba da shawara ga sarakuna da
mataimakansu bisa ga abinda ya shafi fassarar Kur'ani kada su bar wanda
sharuddan yin tafsiri da wa'azi basu cika gareshi ba, ya rika yin tafsiri da
wa'azi cikin jama'a. Su kuma masu iznin yin tafsiri da wa'azi su gujema abinda
zai kawo tashin hankali.
Wannan abinda wadannan malamai suka yi ittafaki a kansa an
sake tattauna shi a gaba gareni nan Sokoto ranar Litinin 26/2/1979 tare da wasu
Sarakuna da Manyan Malamai daga Jihohi dabam dabam.
Duk wadanda suka halarci wannan taro sun yi ittifaki game da
abinda wannan Kwamitin Malamari ya gabatar. Kuma sun rokeni in sanarda ku, don
ku kuma ku sanar da sauran jama'a birni da kauye da kuma sauran malaman da basu
sami damar halarta ba domin su yi ma mabiyansu bayani akan wannan abin farin
ciki na ittafakin malamai na karfafa abinda zai jawo zama Iafiva a tsakanin
Musulmi kuma da gujewa abinda zai kawo tashin hankali.
Duk wani wanda ya saba ma wannan
ittifaki, shi ne mai neman jawo fitina a tsakanin Musulmi. Sai a gabatar da shi
a gaban 'Yan Sanda akan yana neman kawo tashin hankali ga Kasa.
Mun sa wani Kwamiti don shi tsara
sharuddan da za'a ajive kafin a ba wani mutum iznin yin wa'azi. Za mu aiko muku
muku nan da nan da an kare shi.
Allah shi
taimakemu 'bisa taimakon Addininsa, Amin.
Haza Wassalamu.
(SARKIN
MUSULMI)
za mu ci gaba.... . daga inda Abubakar Gumi ya warware Alkawari
No comments:
Post a Comment