Gabatarwa
Godiya ta tabbata ga Allah Madaukakin
Sarki wanda yake cewa ku yi riko da
igiyar Allah gaba daya kada ku rarraba.
Tsira da aminci su
tabbata ga Shugabanmu Annabi muhammadu (S.A.W) wanda yake cewa: "Wanda ya
ga abin ki daga cikin ku ya kawar da shi da hannunsa, idan ba zai iyaba ya yi
da bakinsa, idan ba zai iyaba ya ki abin a Zuciyar sa wannan shi ne mafi raunin
Imani".
Allah ya
yarda da magabatan da suka tafi akan tafarkinsa madaidaici, da masu yin koyi
das u har zuwa ranar tashin kiyama.
Bayan haka wannan takaitaccen bayani mai zuwa a cikin
wannan (GABATARWA) littafi na faroko cikin jerin littafinmu mai suna: (TUSHEN
WAHABIYANCI A NaJERIyA) wata karamar
shimfida ce wacce za tayi wa mai karatu jagoranci zuwa ga wani sako wanda muke
fata mai karanta wannan littafi ya fahimta daga karshe cewa "akwai wasu
mutane da suke ta yunkuri wai sai wannan kasar ta rungumi akidar Wahabiyanci a matsayin akidar ko wane musulmi
kamar yadda abin yake a kasar Saudiyya" in ba haka ba kuwa ba sauran zaman
lafiya.
A wajen kokarinmu na muyi ma 'yan'uwa musulmai takaitaccen
bayani a rubuce, sai muka ga ya kamata mu faro bayani tun daga farkon shirye-shiryen da aka fara
gabatarwa a matsayin asasi na ginin wannan akida ta wahabiyanci don ganin ta ci
gari da yaki kama tun daga rubutun
rahoto har zuwa fassara kur'ani, da buga littafai kanana da manya , da kafa kungiyoyi,
da gangamin wa’azi kamar haka:
-
Rubuta kananan jawabai a
jaridu kamar yadda yake a jaridar Gaskiya ta fi Kwabo da wasu jaridu na Hausa
da Turanci.
-
Rahotanni na sakamakon
bayan tarurruka.
-
Koyarwa ta hanyoyin
sadarwa (Redio - Kaset na sauraro da na ji da gani).
-
Rubuta littafai, farawa
tun daga rubuta kananan Makaloli har zuwa ga tafsiri, da sauran wasu littafai.
-
Kafa kungiyoyi da yin
gangamin wa’azi daga gari zuwa gari.
Wadannan ginshikai guda hudu sune aka
dogara da su wajen dora ginin akidar a kansu, kuma akan su ake so kowane
musulmi ya dora nashi ginin. Ganin shirin nasu ya fara ne da rubuta kananan
jawabai har zuwa fassara kur’ani da Hausa da Larabci da Turanci domin cimma
manufa, ganin haka shine tarko mafi inganci wajen kama musulmi- kamar yadda bayani zai zo – shi ne muka
ce bari mu sa mai karatu a hanya shima domin ya fara da abinda shirin samarma akidar
Wahabiyyanci gindin zama ya fara, kafin mu ja mai karatu zuwa ga yin tsokaci a
cikin “Raddul Azhan”. Da yin bayani a kan maudu’ai daban daban in Allah Ya
yarda.
Wannan
littafi mai suna Gabatarwa kamar duwatsu ne na ginin da za mu yi a littafai na
gaba masu zuwa, kamar yadda za mu gani a cikin littafin takaitattun bayanai ne
na rahotannin taruka, da tattaunawa a jaridu irin su Gaskiya ta fi Kwabo da jaridar
Amana da Makaloli da bayanan rediyo, kuma munyi kokarin kawo shekaru wani
lokaci har da wata da ranar da aka buga jaridun da muka kawo wani bayani mai
tushe irin wannan saboda masu tsokaci a kan irin wadannan bayanai domin
tabbatar da gaskiyar abinda ya faru, wannan shi ya sa za mu fara da bayanin
taro kamar haka:
No comments:
Post a Comment