Tuesday, July 31, 2012

Gabatarwa (2)



TARON JAMA’ATU NA 14/08/2009
A taron da aka yi ranaku biyu a dakin taro na Jama’atu Nasril Islam a Kaduna, a ranakun Juma’a da Asabar na 14/08/2009 da 15/04/2009 wanda Mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Sa’adu Abubakar ya Jagoranta, domin tattauna wasu muhimman abubuwa.
abubuwan da aka tattauna muhimmai guda biyu ne:
1.      maganar ganin watan azumi, saboda alokacin mako guda ya rage a dauki Azumin watan ramadan.
2.      sai kuma batun masu yin Tafsirai a watan azumi ana sawa a gidajen Rediyo, a yi masu nasiha  da su rinka fadar abin da Allah ya ce su  daina sa son zuciya suna sukan juna da kafirta Musulmi.
Allah ya saka ma shugaban taro da alhairi da sauran Sarakuna da malamai da manyan ma’aikata da sauran jama’ar da suka halarci wurin wannan taro da niyya mai kyau.
Sai dai a wurin wannan taro da aka fito da sakamako mai kyau, ko da shike ba a yi la’akari da batuncin da ake yi a tafsiran da ake sawa a gidajen rediyo na yau da kullum ba, na wadanda suke raye  da wadanda suka mutu.
Har ila yau da rubutaccen tafsirin Hausa, da na Larabci, na Malam Abubakar Gumi, wanda ya tara wadannan maganganu na batanci, wanda shi almajiran Malam Abubakar Gumi suke dubawa su fassara, su yi sharhi da abin da suke cira daga bakinsa a kullun.
Tare da cewa a wannan karon kamar an dauki tsattsauran mataki na yin gyara, amma sai tsawatarwar ta zamo kamar an kara ma tabo ruwa ne, don kuwa har sabbin masu batancin aka karo, suna cewa babu wanda ya isa ya hana su fadar abin da -wai- Allah ya ce.
Allah ya sani wasu wadanda ake sa tafsiransu a gidajen rediyo wadanda da ma ba a san su da batunci ba, sai dai kokarin kare kai, suna iyakacin kokarinsu a wurin tafsiransu, Allah ya kara ba su hakuri, don kuwa mun san sun yi shiru ne don martaba kiran da Mai alfarma Sarkin Musulmi da sauran sarakuna suka yi, da kuma kokarin da a ke yi a kullum don samun hadin kai a tsakanin musulmi, ba a Najeriya ba kawai a duk kasashen Musulmi na duniya don magance fitintunun da suka shama kowa kai wanda ake jinginawa ga Musulmi. Allah ya sauwake.
Amma ya kamata shuwagabanninmu su sani cewa magance rikici a tsakanin malamai a kasar nan ba abu ne mai sauki ba, don ya riga ya sami gindin zama a tsakanin al'umma, kuma wasu suna cin gajiyarsa, don haka ya zama dole mu dauko dan takaitaccen tarihinsa, da bayanin inda aka bi aka bibbirne shi a cikin wasu tafsirai kamar  "رد الأذهان" na Malam Abubakar Gumi, da sauran wasu littafai irin shi, don a tono shi a nuna ma Jama’a inda cutar take.
Kafin mu shiga cikin wannan tafsiri yana da kyau mu dan tabo tarihin wannan harka ta Wahabiyanci yanda ta shigo kasar nan, da kuma yanda Allah Madaukakin Sarki ya tsare kasarmu, daga irin abin da ya sami Al’ummar Musulmi a kasar Hijaz kafin a canza mata suna zuwa kasar Saudiya. 
halin zamantakewa A shekarar 1962 zuwa 1965
Dr. Ahmad Gumi ya taba fadi a wurin tafsirinsa na shekara ta 2006 cewa: “Mahaifinsa Malam Abubakar Gumi, shi da Firimiyar Jihar Arewa Mai Girma Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto sun hada hannu don kawo gyara a cikin Addinin Musuluci sai Kafirai suka kashe shi”.
Da ya ke Dr. Ahmad Gumi ya tabo tarihi, kuma ta yiwu labari aka ba shi, don lokacin yana karami, kuma harkar gwagwarmayar Musulunci daga baya ya kutsa kai a ciki da rana tsaka, kuma kasancewar almajiran mahaifinsa yawancinsu yara ne irinsa, kuma ga alama bai bi wadanda a ka yi abin da su ba don ya san gaskiyar al’amarin saboda fahimtar su ta addini ba daya ba ce.
Saboda haka sai muka ga tunda ga wata gaba ta samu ta neman gyara, wanda sai an san ciwo za a san maganinsa, sai muka ga ya dace mu gaya masa abin da bai sani ba, don kar mu shiga cikin fushin da Allah ya keyi da masu boye Ilimi, don ta haka za a gane tuni aka gama gudu, a yanzu zamiye a ke yi.
Ba za mu koma ga tarihin yanda aka kafa daular Wahabiyanci a kasar Hijaz ba, wanda a yanzu ake kiranta da suna kasar Saudiya, a zamanin Sarki Abdul-Aziz, wanda aka hallaka dubban musulmi musamman Ahlul-Baiti a garin Makka da Madina - bayin Allah wadanda aka zarge su da bauta ma kabarurrukan salihan bayi mun san Dr. Ahmad Gumi yana da wannan tarihi duk da a na boye shi a Saudiya ba su son a bayyana irin tabargazar da suka yi domin yada sharri ba shi da kyau a addinance.
Shi Malam Abubakar Gumi wanda yake da ra’ayin Wahabiyanci, a shekara ta 1962 aka nada shi Alkalin-alkalai na Jihar Arewa, shekara guda bayan da aka nada shi, ya ba  Firimiyar Jihar arewa Mai Martaba Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto shawara da a shirya taron malamai na Arewa don tattauna wasu matsaloli kamar yadda bayaninsa a wurin taron ya nuna.
An yi wannan taro na farko a Ranar 23/08/1963 wanda aka yi kwanaki uku ana yi, malaman da aka gayyato zuwa wurin wannan taro (47) ne amma malamai biyu ne kawai ba su sami halarta ba. Shugaban taro shine Wazirin Sokoto Shaykh Malam Junaidu, babban bako mai jawabi shine Firimiyan Jihar Arewa Alhaji Sir Ahmadu Bello Sardauna.
Abubuwan da aka tattauna a wurin taron sune: Maganar Hajji, Zakka, Sadaki, da Azumi, ga kadan daga jawabin Mai Martaba Sir Ahmadu Bello a wurin wannan taro inda yake cewa:
Bambancin darika, ko na Mazhaba ba zai hana mu taruwa wuri daya mu duba abin da zai kyautata addininmu ba, kamar yadda bai hana mu haduwa a masallatan Juma’a da sauran Masallatai ba, haka nan bai hana mu haduwa a sauran wurare na ma’amalar yau da kullum ba.
Ta haka ne Musulmi suka kange Addininsu daga sukan wasunsu, darikoki da Mazhabobi sun banbata da Juna, amma manufar su duka guda ce”.
Wannan wani yanki ne daga jawabin Alhaji Sir Ahmadu Bello Sardauna, Allah ya saka masa da alhairi, wannan jawabi yana nuna halin zamantakewar al’ummar Musulmi a shekara ta (1963) yadda ‘Yan darika da wadanda ba ‘yan darika ba suke zaune lafiya, suke yin sallah a Masallaci daya. A gaban Malam Abubakar Gumi aka yi wannan jawabi.
Amma sai ga shi a cikin shekaru biyu kacal al’amura sun canja, a taron malamai na biyu da aka yi a shekara ta 1965 wanda aka kira malamai (101) duk da shugaban taro wazirin Sokoto Shiekh Junaidu, Allah Ya gafarta masa, amin.
Ajandar taro magana ce a kan kabalu da Sadalu da kuma maganar darikoki, da maganar mayaudaran malamai, da masu tafsirin kur’ani da barna da maganar jahilan masu wa’azi, da maganar barin aiki da littafan malaman Sunna, da maganar tarbiyya batacciya da ta asali, da bincika malamai masu haddasa fitina.
Daga jin yanda ajandar taron ta koro; tana  nuna alfijir din Wahabiyanci ya fara kunno kai a kasar nan, don haka sai kiyayewan Allah don idan aka gwama ajandar da jawabin da Mai Martaba firimiyan Jihar Arewa Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto ya yi, za a gane tafiya ta fara sauyawa.
Zamu kawo kadan daga cikin abinda yace a wata doguwar huduba da yayi a Ranar Talata 15 ga watan Yuni 1965 wanda yayi dai dai da 14 ga watan Safar Hijira 1385, Jawabin wanda aka rubuta da hausa yana da sadara (152) ga kadan daga cikin wannan Jawabin wanda yafi tsorata Mahalarta wannan taro:

Malik bin Anas ya ce: Ya halasta a kashe Sulusi watau Kashi daya daga uku na Jama’a masu fitina, domin kashi biyu su rayu cikin kwanciyar hankali.
Idan muka ji dokokin da aka fito da su a karshen taron, za a iya gane wadanda a ke zargi da kawo fitina a wannan lokacin, an dai kafa dokokin ne kamar haka:
-          an hana ko wane limamin da zai jagoranci Sallah, tare da jama’a yayi kablu, idan ya ki bari za a cire shi.
-          an hana Malamai kai ziyarce-ziyarce wajen muridan su, in suna son wani abu, sai muridai su tafi su iske su.
-          An hana tarbiyya wanda ake yin tawassuli wanda ya yi da wanda ya sa aka yi sun kafirta.
-          An hana yin tafsiri da wa’azi sai wanda aka jarraba shi ya ci jarabawa….
Abubuwa goma shadaya ne aka cimma matsaya a kansu na karshensu shine: Hana ginin Masallatai barkatai”. 


  JUYIN MULKIn soja na faroko a najeriya NA 1966
Bayan wadannan Dokoki da aka kafa sun fara aiki da wata shida, sai kasa ta fada cikin wata fitinar, wato juyin mulki na sojoji, wanda ta kai ga sanadiyyar rasuwar Firimiyar Jihar Arewa Sir Ahmadu Bello Sardauna a shekara ta 1966, Allah ya gafarta masa Amin. wannan juyin mulki ya jawo yakin (Biyafara) na kusan tsawon shekaru uku.
Wannan hali da kasa ta shiga sai ya kawar da hankali ga batun Sallar kablu da maganar Tarbiyya da maganar shayhunai masu kawo ziyara, sai aka mayar da hankali wajen neman hadin kan al’ummar Jihar Arewa, da na Jihar Yamma, ba tare da yin la’akari da wannan musulmi ne ko wannan ba musulmi ba.
Bayan an karkasa Gwamnatin Jihar Arewa zuwa Jihohi guda 5 an soke tsarin En’e-En’e wanda ya takaita ikon sarakuna a sha’anin mulki, sai ya zama ko wace jiha tana cin gashin kanta, tare da sarakunanta, wadanda aka canja masu suna zuwa Sarakunan Gargajiya, a maimakon Sarakunan Musulunci, amma Malam Abubakar Gumi, an barshi a matsyin Alkalin-Alkalan Jihohin Arewa.
Jama’atu Nasril Islam mai helkwata a garin Kaduna, wanda Firimiya Sir Ahmadu Bello Sardauna ya kafa a shekara ta 1961 Allah cikin ikonsa ya sa ba a ci gajiyarta ba, sai bayan rasuwarsa, inda ta zama ita ce cibiya guda daya tal da ta saura don hada kan al'ummar Musulmi na jihohin Arewa, a karkashin sarkin Musulmi Alhaji Sir Abubakar na uku, tare da sarakunan jihohin Arewa, da manyan malamai, da wasu daga cikin ma’aikatan Gwamnati masu sha’awar bayar da gudummuwa a harkokin musulunci.
Wannan kungiya wanda a cikin kudurorinta duk mai cewa: “Lailaha Illallahu, Muhammadur Rasulul Lahi” dan ta ne, ko wace irin mazhaba yake bi, ko wace irin darika yake yi, samun wannan kungiya ta Jama’atu ya samar da kyakkyawar fahimta tsakanin malamai da sarakuna, amma bai kawar da irin tsanar da ake yi wa almajiran Shayhu Ibrahim Kaulaha ba, sai da Gwamnatin tarayya a karkashin Janaral Yakubu Gawan a shekara ta 1968 ta tura wata tawaga ta musamman a karkashin jagorancin Malam Aminu Kano zuwa Kaulaha a kasar Senigal wurin Shayhu Ibrahim (R.A) don neman a yi wa Najeriya du’ai ta sami galaba a kan ‘yan tawaye a kawo karshen yakin Biyafara.
wannan ziyara ya haifar da sake kulla sabuwar alaka da Gwamnatin Gawan ta yi da Shayhu Ibrahim Kaulaha (R.A) kuma ya kawar da karan tsanar da ake sa wa almajiransa masu yin Sallar kablu a wancan lokacin, da ci gaba da kawo ziyarar shaihunnai da sharifai zuwa kasar nan wanda aka hana a shekara ta1965.
A sakamakon haka ne Shaykh Malam Ummaru Sanda limamin Sojoji a garin Kaduna daya daga cikin jamian gudanarwa na Jama’atu Nasril Islam ya rubuta wata makala a shekara ta (1968) mai dauke da taken: MATSAYIN kABLU DA SADALU A CIKIN AL-kUR’ANI DA SUNNAR MANZON ALLAH mai shafi (18) wanda aka rika bugawa a cikin Jaridar gaskiya ta fi Kwabo ta wannan shekarar, wannan jawabi na Malam Ummaru Sanda ta jawo mayar da martani daga malamai a jaridu da littafai, musamman saboda in da ya nuna yin sallar kablu ita ce sunnar da tafi shahara.
Tare da cewa wannan jawabi na Malam Ummaru Sanda ta kawar da kyamar da ake yin ma masu yin sallar kablu, sai dai kuma ta sanya an bude wani sabon shafin na shiga cikin darikar Tijjaniya ita kanta, domin a jawabin rufe muhawara, wanda Kanfanin buga jaridar Gaskiya ta fi Kwabo ta dauki alhakin kawo muhawarorin ta nuna cewa za ta rufe wannan muhawara da ra’ayin Malam Abubakar Gumi ne a matsayinsa na Alkalin-Alkalan Jihohin Arewa.
A jawabinsa wanda aka buga  a shafi na (9) na jaridar Gaskiya ta fi Kwabo ta ranar Litinin (4) ga watan Oktoba, 1971, mai dauke da taken: kabalu da sadalu ko wannen su yana da asalinsa.
Bayan ya fadi hujjojinsa a game da kabalu da sadalu, sai a karken jawabin ya jawo hankalin wasu jama’a da cewa:
Mai sharia Malam Bashir Sambo - Allah ya gafarta masa amin - ya fada a wata hira da Jaridar Gaskiya ta fi Kwabo ta yi da shi a ranar 22/08/2005 a shafi na 12 da 13 a fira ta 4 game da farkon rikicin darika da Malam Abubakar  Gumi, ya nuna cewa yana tare da Malam Gumi a Jama’atu Nasril Islam tun a shekara ta (1968) ga abin da ya ce ya fara jawo rikicin:
To ka san yadda abubuwa suka faro tun asali, mutane ba su gane ba, lokacin da shi Sheikh Gumi ya ke Grand Kadi ya samu dama ta yin wa’azi da sauransu, ya nemi ya yi amfani da fahimtarsa, rigimar da aka fara yi ita ce, lokacin da yake wa’azi a masallacin Sarkin Musulmi Bello, inda ya yi maganar Jauharatul Kamali yace Surguduballe ce, musamman kan wata kalma “ASkAM” wannan shi ne farko farin rikicin da ya fito
Wannan shi ne jawabin Malam Bashir Sambo, idan an duba jaridar ta shekarar 1968 za a ga inda Malam Abubakar Gumi ya ke cewa da za a canja wannan kalmar a ce"صراطك تم المستقيم" da babu aibi a karanta wannan salati a cikin wazifa.
Sai dai malamai sun maida masa da martani game da wannan kalma ta"الأسقم" daga cikin wadanda suka mayar da martani akwai Shaykh Malam Atiku Kano wanda ya rubuta littafi mai suna:
 "تنبيه النبهاء ليلاً يغتروا بأقوال السفهاء".
Wanda ya kulle kofar muhawara game da wannan kalma ta "الأسقم" shine shayhin Malamin Larabci a Jami’ar Bayaro ta Kano prof. Aliyu Na’ibi Suwaid, a inda ya rubuta Littafi mai suna:
"تعليق لغوي على كلمة الأسقم الواردة في الصلاة المعروفة بجوهرة الكمال"
            Jawabin da ya yi a wannan dan karamin littafi wanda a ka buga a shekara ta 1977 wanda ya yi daidai da (1409) Hijiriyya ya rufe bakin Malam Abubakar Gumi, bai sake magana a kan wannan kalmar ba, tare da cewa bai kawo karshen rigimar ba, don manufar shi a koma ne gaba daya, a rungumi akidar Wahabiyanci a wannan kasa wanda aka so a baya a yi amfani da Mai Martaba Firimayar Jihar Arewa don yada ta.
            A shekara ta (1970) Malam Abubakar Gumi ya wallafa wani littafi mai suna: "العقيدة الصحيحة" daga sunan da aka sanya ma wannan littafi za a fahimci cewa; a na shirin kawo ma al'ummar Musulmin kasar nan wata sabuwar fahimta ce game da Ilimin Tauhidi sabanin ta Imamul Ash’ari wanda su ka rayu a kanta wanda ita ce mafi yawan kasashen Musulmi su ke kai, in banda kasar Saudiya dmai bin sabuwar akida ta dan Abdul-Wahabd.
Sai dai wannan littafi wanda a ka so ya zama abin yin aiki da shi a Makarantun Zaure da na Nizamiya Allah bai sa ya sami karbuwa ba, domin hatta a wurin almajiran malamin littafin na shan suka saboda dalilai masu dama.
Har ila yau malamai da yawa sun kalubalanci wannan littafi saboda dinbin kurakuran da ya taras a ciki, a maimakon akidar da littafin ya kunsa ya zama sahihi, sai ya zama fasidi, kamar yadda Shaykh Malam Sani Kafanga ya rubuta wani littafi don yin raddi ga wannan littafin ya fada : "المنح الحميدة في الرد على فاسدة العقيدة" mai son karin bayani sai ya nemi wadannan littafai guda biyu da na Malam Abubakar Gumi da na Shaykh Malam Sani Kafinga, Allah ya gafarta masa, amin.
            Malam Abubakar Gumi a kokarinsa na tabbatarda Wahabiyanci da shafe darikar Tijjaniya a doron kasa, a shekara (1973) a wurin Karatunsa an yi masa tambaya game da karanta Salatil Fatihi sai ya karanta sannan yace: "Wannan salatin Annabina lafuzzanta masu kyawuna, sai dai cewa da a ke yi an yi ma Ahmadul Bakariy wahayinta shi dai ak kahirci, da kuma cewa karanta ta yahi karanta Al-kur’ani, ku duba cikin littafin Jawahirul Ma’ani”.
            Da farko kamar yanda muka fadi a baya Malamin ya fara ne da kalmar (Al-askam) ta cikin (Jauharatul Kamali) inda ya yi gyara ya ce da za a ce"صراطك المستقيم" da yafi, a lokacin (Salatil Fatihi) bai ce ga aibin ta ba sai anan, shima anan ba cewa a ka yi karanta ta yana da aibi ba, imma da shi ba a riga an gano ba a lokacin.
            To, amma duk da haka wannan jawabin na sa, ya jawo ka-ce na-ce da shi Malamin, har da wadanda ba ‘yan darikar ba abokan aikinsa a Jama’atu Nasril Islam, kamar mai shari’a Malam Bashir Sambo, wanda ya fadi a wata hira da Jaridar Gaskiya ta fi Kwabo ta yi da shi ta ranar 24/08/2005 a shafi na (13) a inda yace:
Na taba daukar Jawahirul Ma’ani na tafi wajen Malam Gumi lokacin da ake rigimar Salatul Fatihi” ko saukakkiya ce ko kuma wanda ya karanta ta yana da lada kaza.
            Na nuna masa wani shafi da aka yi bayanin falalarta, wanda  a karshen falalar sai aka ce, mai yiwuwa ne wani wanda ganewa ba ta ishe shi ba ya ce:  wannan salatin ita zai ta’allake mata, tun da ta fi kur’ani, ya ce ko da aka yi maganar falala, babu yadda za ayi salatil fatihi ta fi kur’ani, ba wani abin da ya fi kur’ani, a cikin littafin a ka fadi haka..”
Ya ci gaba yana tambayar Malam Abubakar Gumi da cewa: me ya sa ba a karanta komai har karshe don mutane su amfana?”
Wannan ita ce magana ta adalci, daga bakin malami adali mai shari’a Malam Bashir Sambo Allah ya yi masa gafara, hirar da a ka yi da shi ta na da tsawo, sai dai kawai a nemi jaridan har ya kawo masa misali da yanda ya ke yawan son a karanta (Salatun Tunajjina) alhali duk jirgi daya ya kwaso su da Salatil Fatihi, har ma Salatil Fatihi ta dara don an san wanda aka ruwaito daga gareshi.
CIRE MALAM GUMI A ALKALIN ALKALAI  A shekara ta 1975
Sauke Malam Abubakar Gumi a Matsayin Alkalin Alkalai na Jahohin Arewa a shekarata (1975)ya sa ya rasa wata dama da ya ke da ita ta fadar abin da ya ke so, ba tare da jin komi ba, saboda kariya da yake da ita ta huskan jami’an tsaro. da kuma alkalai da su ke karkashinsa, saboda haka sai ya yi kokarin samar da wata kungiya ta ‘yan bangarsa a shekare ta (1976), shi da kansa Malam Abubakar  ya taba gaya ma wani babban mai sarauta, da ya tambaye shi dalilin kafa kungiyar Izala, sai ya gaya masa cewa ya sa an kafata ne don ta rika bashi kariya saboda ya ga ‘yan darika suna barazanar hallaka shi.
Babu shakka wannan kungiya ta Izala ta bayar da kariya ga Malam Abubakar Gumi ta wajen yada Akidar Wahabiyanci a wannan kasa, don ta fito da karfinta, ba ta shakkar fadar duk abin da ta ga dama.  Misali a wurin wani taro da Jama’atu Nasril Islam ta kira a shekara ta (1977) Alhaji Bala Sirajo daya daga cikin jagororin kungiyar Izala na hannun dammar Malam Abubakar Gumi ya tashi a taron jama’a ya wanke wa sarakunar da suka halarci taron hannu a ka, babu bakar maganar da bai fada masu ba, wanda ya tayar da hankulansu, amma a karshe sai a ka tsayar da shawarar cewa a jawo su ne, don a tafi tare da su a cikin harkokin Jama’atu, wanda ya kara masu karfin guiwa, sarakuna suka shiga jin tsoransu.
__________________________________________
za mu tashi a
DUBA YANDA ZA A SAMI MATSAYA A 1977/ 78


 
 

Monday, July 30, 2012

Gabatarwa

Gabatarwa 

Godiya ta tabbata ga Allah Madaukakin Sarki wanda yake cewa  ku yi riko da igiyar Allah gaba daya kada ku rarraba.

 Tsira da aminci su tabbata ga Shugabanmu Annabi muhammadu (S.A.W) wanda yake cewa: "Wanda ya ga abin ki daga cikin ku ya kawar da shi da hannunsa, idan ba zai iyaba ya yi da bakinsa, idan ba zai iyaba ya ki abin a Zuciyar sa wannan shi ne mafi raunin Imani".
Allah ya yarda da magabatan da suka tafi akan tafarkinsa madaidaici, da masu yin koyi das u har zuwa ranar tashin kiyama.
Bayan haka wannan takaitaccen bayani mai zuwa a cikin wannan (GABATARWA) littafi na faroko cikin jerin littafinmu mai suna: (TUSHEN WAHABIYANCI A NaJERIyA) wata karamar shimfida ce wacce za tayi wa mai karatu jagoranci zuwa ga wani sako wanda muke fata mai karanta wannan littafi ya fahimta daga karshe cewa "akwai wasu mutane da suke ta yunkuri wai sai wannan kasar ta rungumi akidar  Wahabiyanci a matsayin akidar ko wane musulmi kamar yadda abin yake a kasar Saudiyya" in ba haka ba kuwa ba sauran zaman lafiya.
A wajen kokarinmu na muyi ma 'yan'uwa musulmai takaitaccen bayani a rubuce, sai muka ga ya kamata mu faro bayani  tun daga farkon shirye-shiryen da aka fara gabatarwa a matsayin asasi na ginin wannan akida ta wahabiyanci don ganin ta ci gari da  yaki kama tun daga rubutun rahoto har zuwa fassara kur'ani, da buga littafai kanana da manya , da kafa kungiyoyi, da gangamin wa’azi kamar haka:
-          Rubuta kananan jawabai a jaridu kamar yadda yake a jaridar Gaskiya ta fi Kwabo da wasu jaridu na Hausa da Turanci.
-          Rahotanni na sakamakon bayan tarurruka.
-          Koyarwa ta hanyoyin sadarwa (Redio - Kaset na sauraro da na ji da gani).
-          Rubuta littafai, farawa tun daga rubuta kananan Makaloli har zuwa ga tafsiri, da sauran wasu littafai.
-          Kafa kungiyoyi da yin gangamin wa’azi daga gari zuwa gari.
Wadannan ginshikai guda hudu sune aka dogara da su wajen dora ginin akidar a kansu, kuma akan su ake so kowane musulmi ya dora nashi ginin. Ganin shirin nasu ya fara ne da rubuta kananan jawabai har zuwa fassara kur’ani da Hausa da Larabci da Turanci domin cimma manufa, ganin haka shine tarko mafi inganci wajen kama musulmi- kamar yadda bayani zai zo – shi ne muka ce bari mu sa mai karatu a hanya shima domin ya fara da abinda shirin samarma akidar Wahabiyyanci gindin zama ya fara, kafin mu ja mai karatu zuwa ga yin tsokaci a cikin “Raddul Azhan”. Da yin bayani a kan maudu’ai daban daban in Allah Ya yarda.
            Wannan littafi mai suna Gabatarwa kamar duwatsu ne na ginin da za mu yi a littafai na gaba masu zuwa, kamar yadda za mu gani a cikin littafin takaitattun bayanai ne na rahotannin taruka, da tattaunawa a jaridu irin su Gaskiya ta fi Kwabo da jaridar Amana da Makaloli da bayanan rediyo, kuma munyi kokarin kawo shekaru wani lokaci har da wata da ranar da aka buga jaridun da muka kawo wani bayani mai tushe irin wannan saboda masu tsokaci a kan irin wadannan bayanai domin tabbatar da gaskiyar abinda ya faru, wannan shi ya sa za mu fara da bayanin taro kamar haka: